fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Jami’an Civil Defence sun kama mai garkuwa da mutane a Gombe

Date:

Jami’an tsaro na Civil Defence, sun kama wani matashi dan shekara 25 da ake zargin mai garkuwa da mutane ne dan asalin karamar hukumar Shongom a jihar Gombe, bisa zarginsa da yunkurin yin garkuwa da wani mutum mai suna Usman Mohammed dan shekara 70 a garin Koburga da ke iyaka da Billiri, karamar Hukumar Kaltungo.

Rahotanni ya nuna cewa, Lawal ya yi wa wanda abin ya shafa raunuka daban-daban a sassan kunne da kafada.

Da yake gabatar da wanda ake zargin a ranar Talata, Kwamandan jihar Waziri Goni ya bayyana wanda ake zargin Lawal a matsayin mai garkuwa da mutane wanda ya baiwa jami’an tsaro wahala a baya, inda ya kara da cewa, ya yi barna da ā€˜yan kungiyar sa.

Goni ya bayyana cewa, rundunar ta samu nasarar dakile harin ne ta hanyar hadin gwiwar mazauna yankin, inda ya bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen samar da sahihin bayanai da za su sa jihar ta samu zaman lafiya.

A cewar Kwamandan, Lawal ya gudanar da aiki a kewayen Shongom, Billiri, da Kaltungo. Ya kama mutane ana neman kudin fansa da kisa.

ā€œSauran ā€˜yan kungiyar, kusan hudu, sun gudu da bindigogin AK-47 da wasu bindigu. Su ne ’yan banga da ke yawo a cikin babban birnin Gombe, sun ba jami’an tsaro ciwon kai. Alhamdu lillahi muna da daya daga cikinsu da wasu kusan shida a gidan yari, sauran hudu kuma da yardar Allah za mu same su,ā€ inji shi.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tsohon sakataren gwamnatin a mulkin Buhari ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, SGF, Babachir Lawal ya fice...

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheʙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaʙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunʙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ʙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ʙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...
X whatsapp