Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, a ranar Juma’a ta kama wasu makudan kudade har Naira miliyan 32,400,000 a Legas.
Ana zargin kudaden an ware su ne domin sayen kuri’u a Legas, kamar yadda Wilson Uwujaren, shugaban yada labarai na EFCC ya bayyana.
Kakakin ya tabbatar da cewa an kai wadanda ake zargi da hannu a hannu domin ci gaba da yi musu tambayoyi.
Karanta Wannan: EFCC ta tura jami’anta wajen zaben 2023
Shugaban Hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa ya roki dukkan jami’an da aka tura domin sa ido kan zaben da su nuna jajircewa.
Bawa ya gargade su da cewa kada su ba wa marasa kishin kasa damar yin zagon kasa a zaben da za a yi ta hanyar ba da kudi.
Hukumar ta sanar da cewa, a halin yanzu akwai tawaga masu dabara a dukkan jihohin tarayya da kuma babban birnin tarayya Abuja.
Uwujaren ya kara da cewa “An riga an yada layukan wayar tarho ta kafafen sada zumunta na zamani domin jama’a su raba bayanai game da matsalar kudi,” in ji Uwujaren.