fidelitybank

Da Dumi-Dumi: INEC ta cire sunan Alhassan Ado Doguwa daga wanda ya ci zabe

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta cire sunan shugaban majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa daga jerin sunayen wadanda suka lashe zaben.

Hukumar zabe ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi a mazabar Doguwa/Tudunwada da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu.

Jami’in da ya lashe zaben, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai a baya ya bayyana cewa Doguwa na jam’iyyar APC ya samu kuri’u 39,732 inda ya kayar da abokin hamayyarsa Yushau Salisu Abdullahi na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) wanda ya samu kuri’u 34,798.

Amma a cikin sabbin zababbun mambobin da aka fitar, sunan Doguwa bai fito fili ba.

Idan dai za a iya tunawa, biyo bayan rikicin zabe da aka samu a mazabar bayan kammala zaben, ā€˜yan sanda sun cafke Doguwa bisa zarginsa da hannu wajen kashe wasu mutane da kuma kona sakatariyar jam’iyyar NNPP, zargin da dan majalisar ya musanta da kakkausar murya.

Rundunar ā€˜yan sandan ta tabbatar da cewa akalla mutane uku ne suka mutu yayin da aka kona sakatariyar yakin neman zaben jam’iyyar NNPP da ke Tudunwada tare da kona mutane biyu har lahira.

Daga nan ne aka gurfanar da Doguwa a gaban kotun majistare kan zargin kisan kai, kone-kone da kuma mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, daga bisani aka tsare shi a gidan yari.

Sai dai wata babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Litinin din da ta gabata ta amince da belin dan majalisar kan kudi naira miliyan 500, amma ta hana shi shiga mazabarsa a zaben gwamnoni da na ā€˜yan majalisar jiha da ke tafe.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ʙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ʙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ʙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaʙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ʙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa Ę“an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ʙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ā€˜Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ā€˜Operation Rising Lion’,...
X whatsapp