Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta cire sunan shugaban majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa daga jerin sunayen wadanda suka lashe zaben.
Hukumar zabe ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi a mazabar Doguwa/Tudunwada da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu.
Jamiāin da ya lashe zaben, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai a baya ya bayyana cewa Doguwa na jamāiyyar APC ya samu kuriāu 39,732 inda ya kayar da abokin hamayyarsa Yushau Salisu Abdullahi na jamāiyyar New Nigeria Peopleās Party (NNPP) wanda ya samu kuriāu 34,798.
Amma a cikin sabbin zababbun mambobin da aka fitar, sunan Doguwa bai fito fili ba.
Idan dai za a iya tunawa, biyo bayan rikicin zabe da aka samu a mazabar bayan kammala zaben, āyan sanda sun cafke Doguwa bisa zarginsa da hannu wajen kashe wasu mutane da kuma kona sakatariyar jamāiyyar NNPP, zargin da dan majalisar ya musanta da kakkausar murya.
Rundunar āyan sandan ta tabbatar da cewa akalla mutane uku ne suka mutu yayin da aka kona sakatariyar yakin neman zaben jamāiyyar NNPP da ke Tudunwada tare da kona mutane biyu har lahira.
Daga nan ne aka gurfanar da Doguwa a gaban kotun majistare kan zargin kisan kai, kone-kone da kuma mallakar makamai ba bisa kaāida ba, daga bisani aka tsare shi a gidan yari.
Sai dai wata babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Litinin din da ta gabata ta amince da belin dan majalisar kan kudi naira miliyan 500, amma ta hana shi shiga mazabarsa a zaben gwamnoni da na āyan majalisar jiha da ke tafe.