Gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi, ya ce, kwata-kwata bai yi nadamar komawa jam’iyyar APC ba.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a wajen wani gangamin goyon baya da masoyan sa suka gudanar a dandalin ruwa na Udensi da ke Abakaliki, babban birnin jihar.
Ya roki magoya bayan sa da su kwantar da hankula tare da tabbatar wa magoya bayan jam’iyyar cewa, hukuncin tsige shi a matsayin gwamna ba zai tsaya iya nan ba.
A ranar Talata ne mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya bayar da umarnin tsige gwamnan da mataimakinsa Kelechi Igwe saboda sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a watan Nuwamba 2020.
Ya kuma kori ‘yan majalisar dokokin jihar Ebonyi 16, da aka kora saboda sun shiga jam’iyya mai mulki, cewa da su ci gaba da hakuri.
Gwamnan ya ce: “Ba ni da nadamar barin jam’iyyar PDP. Hukuncin da aka kore ni a matsayin gwamnan ku ba zai tsaya a daukaka kara ba, kuma zan ci gaba da zama gwamna kamar yadda har yanzu n ake aiki.