fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Har yanzu bamu fice daga APC ba – Sanata Marafa

Date:

Sanata Kabiru Marafa na jihar Zamfara ya musanta rahotannin da ke cewa, shi da tsohon gwamnan jihar, Abdulaziz Yari sun fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.

Marafa a yammacin Lahadin da ta gabata yayin wata hira da Tambarin Hausa, ya ce; “Abin da muka sani shi ne muna tattaunawa da jam’iyyun siyasa da dama da suka gayyace mu mu shiga cikin su a jihar.”

“A yanzu duk wani labarin da aka ce mun yi murabus, karya ne.”

“Abin da na sani shi ne, akwai jam’iyyun siyasa da dama, ba PDP kadai ba, wadanda suka gayyace mu suna son mu shiga har zuwa yanzu muna tattaunawa da su.”

“A iyakar sanina har ya zuwa yanzu ba mu cimma matsaya da kowa ba…Ba gaskiya ba ne cewa mun koma PDP, duk wanda ya fadi haka ya yi kuskure.”

“A matsayi na, ina kira ga mutane da su yi watsi da duk wani bayani game da batun daga kowane mutum, har sai sun ji ta bakinmu, … Har yanzu ba mu yanke shawara ba.”

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp