fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Gwamnonin G5 na PDP sun tafi Spain a kan rikicin jam’iyyar

Date:

Gwamnonin jam’iyyar PDP da aka fi sani da G5, sun yi tattaki zuwa kasar Spain domin gudanar da wani muhimmin taro a cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar.

Jaridar The Nation ta tattaro cewa gwamnonin sun bar kasar zuwa Madrid ne a daren Juma’a sa’o’i bayan da Gwamnan Ribas ya kara zarge-zarge a kan Shugaban Jam’iyyar Iyorchia Ayu.

Wadanda ke cikin jirgin Wike sune Gwamna Seyi Makinde (Oyo); Okezie Ikpeazu (Abia) da Samuel Ortom (Benue) a matsayin gwamnan jihar Enugu, Ifeanyi Ugwuanyi na iya shiga daga baya.

Ku tuna cewa Wike, yayin wata tattaunawa da manema labarai a Fatakwal a ranar Juma’a, ya kara zarge-zarge a kan Ayu yana mai cewa shugaban jam’iyyar na kasa ba shi da kima wajen jagorantar yakin neman zaben jam’iyyar a 2023.

Bayan kammala zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar, gwamnonin da suka fusata sun dage cewa rashin adalci ne jam’iyyar ta samu shugaban kasa da dan takarar shugaban kasa daga Arewa.

Sun ce har sai Ayu ya ajiye mukaminsa na shugaban jam’iyyar, za su yi watsi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar a zaben 2023.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp