Gwamnonin jam’iyyar APC sun gana da shugaba Buhari a fadarsa da ke Abuja a ranar Laraba, ƙarƙashin jagorancin shugaban gwamnonin kuma gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu.
Gwamnonin sun ce sun tattauna da Bahari kan batutuwa da dama musamman game da babban taron Jam’iyyar na ranar Asabar inda za a zaɓi shugabannin jam’iyyar.
Ganawar na zuwa a daidai lokacin da jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ke ci gaba da fuskantar baraka da rashin jituwa tsakanin jiga-jiganta kan babban taro na kasa da kuma zaben shugabanninta.
Tuni jam’iyyar ta kebe wa yankunan kasar mukamai daban-daban, inda misali aka kebe wa yankin Arewa ta tsakiya kujerar shugaban jam’iyya na kasa.
Shugaban Buhari na kokarin ganin an kauce wa kada kuri’a wajen zaben shugabanni, a maimakon haka yake neman a sasanta tsakanin ‘yan takara, yayin da gwamnonin jihohi ke cewa za su goyi bayan duk wanda shugaba Buhari ya ce a ba kujerar shugabancin jam’iyyar.
Sai dai wasu kusoshin jam’iyyar sun bayyana cewa ba su yarda da wannan tsari ba, kamar tsohon gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari, wanda ya ce, zai ci gaba da fafutikar neman kujerar shugaban jam’iyyar duk da cewa ba yankinsu ne aka kebe wa kujerar ba, kuma a ganinsa bai wa wani yanki ko wani mutum mukamin ba tare da zabe ba, rashin adalci ne.