fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Gwamnonin APC sun tattauna da Buhari a kan taron jam’iyyar

Date:

Gwamnonin jam’iyyar APC sun gana da shugaba Buhari a fadarsa da ke Abuja a ranar Laraba, ƙarƙashin jagorancin shugaban gwamnonin kuma gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu.

Gwamnonin sun ce sun tattauna da Bahari kan batutuwa da dama musamman game da babban taron Jam’iyyar na ranar Asabar inda za a zaɓi shugabannin jam’iyyar.

Ganawar na zuwa a daidai lokacin da jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ke ci gaba da fuskantar baraka da rashin jituwa tsakanin jiga-jiganta kan babban taro na kasa da kuma zaben shugabanninta.

Tuni jam’iyyar ta kebe wa yankunan kasar mukamai daban-daban, inda misali aka kebe wa yankin Arewa ta tsakiya kujerar shugaban jam’iyya na kasa.

Shugaban Buhari na kokarin ganin an kauce wa kada kuri’a wajen zaben shugabanni, a maimakon haka yake neman a sasanta tsakanin ‘yan takara, yayin da gwamnonin jihohi ke cewa za su goyi bayan duk wanda shugaba Buhari ya ce a ba kujerar shugabancin jam’iyyar.

Sai dai wasu kusoshin jam’iyyar sun bayyana cewa ba su yarda da wannan tsari ba, kamar tsohon gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari, wanda ya ce, zai ci gaba da fafutikar neman kujerar shugaban jam’iyyar duk da cewa ba yankinsu ne aka kebe wa kujerar ba, kuma a ganinsa bai wa wani yanki ko wani mutum mukamin ba tare da zabe ba, rashin adalci ne.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp