Gwamnatin jihar Bauchi ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Yelwa da kewaye sakamakon rikicin da ya barke tsakanin kungiyoyin matasa biyu da ke gaba da juna a yankin.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Umar Sanda, wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a yayin da ake tantance lamarin a ranar Asabar, ya ce adadin wadanda suka mutu a rikicin ya haura biyu.
Ya nuna takaicin yadda aka bar wani karamin lamari ya lalace.
CP ya ce: “Gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita kuma mu a matsayinmu na jami’an tsaro a shirye muke mu aiwatar da shi. Da zarar na bar wannan wuri, an fara aiwatar da dokar hana fita.