fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Gwamnati ta tsige mukaddashin Akanta na kasa

Date:

Gwamnatin tarayya ta cire mukaddashin babban akanta Mr. Chukwuyere N. Anamekwe, inda aka maye gurbinsa da Mr. Okolieaboh Ezeoke Sylvis, wanda tsohon darakta ne a tsarin asusun gwamnati na bai-daya, wato, TSA (Treasury Single Account).

Rahotanni na cewa, an maye gurbin mai rikon mukamin na Akanta-Janar din ne saboda hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasar zagon-kasa, EFCC, na bincike a kansa.

A cewarrhotanni, gwamnatiun ba ta ji dadin wasu kalamai da ya yi ba inda ya ce, Najeriya na ranto kudi domin ta biya albashi.

Anamekwe wanda aka nada shi a wannan matsayi na rikon-kwarya a ranar 22 ga watan Mayu bayan da hukumar EFCC ta kama Babban Akantan kasar, Ahmed Idris bisa zargin almundahana da naira biliyan 80, ya yi kalaman cin bashin ne, a ranar 14 ga watan Yuni, na 2022, kuma kwana bakwai daga nan aka cire shi.

Mista. Sylva, wanda ke zaman mukaddashin Babban Akantan a yanzu, rahotanni na nuni da cewa zai yi ritaya a cikin watanni uku na farkon shekara mai zuwa, 2023.

Tuni dai gwamnatin tarayya ta kaddamar da neman wanda za ta nada a matsayin sabon Babban Akantan, kamar yadda bayanai ke nunawa.

Jaridar The Nation ta Najeriyar ta ruwaito cewa, duk wani kokari da ta yi na neman gaskiyar kalaman da Anamekwe ya yi cewa gwamnati na ciyo bashi ta biya albashi, ya ci tura.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke É—auka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da Æ™arfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naÉ—a kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka Æ´anbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe Æ´anbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp