fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Gwamnati ta fara kwashe ‘yan Najeriya daga Sudan

Date:

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da fara kwashe ‘yan Najeriya da suka makale a kasar Sudan, bayan barkewar rikici a kasar da ke arewacin Afirka.

Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama da takwaransa, Karamin Minista Zubairu Dada, ne suka tabbatar da hakan a ranar Laraba yayin da suke yi wa manema labarai karin haske game da abubuwan da ke faruwa game da rikicin.

Onyeama ya bayyana cewa tuni motocin bas na alfarma guda 40 suka sauka a kasar Sudan domin daukar ‘yan Najeriya da ke kasar zuwa Masar inda za a dawo da su gida.

Ya ce ofishin jakadancin Najeriya da ke kasar Sudan da kuma hukumomin hukumar bayar da agajin gaggawa ta tarayya FERMA ne ke gudanar da aikin kwashe mutanen.

A cewar Ministocin, an dauki hayar motocin bas din da ke jigilar ‘yan kasar a kan kudi dala miliyan 1.2, inda suka ce sun hada da kudin samar da tsaro yayin jigilar su zuwa kasar Masar.

Ministocin biyu sun kuma yi nuni da cewa, za a bai wa mata da kananan yara fifiko, ciki har da jami’an diflomasiyya wadanda ke da hannu a cikin ayyukan kwashe mutanen.

Sun yi nuni da cewa gwamnatin Najeriya na yin amfani da yarjejeniyar tsagaita bude wuta na sa’o’i 72 don kwashe ‘yan Najeriya da dama.

Ambasada Dada ya bayyana cewa, tuni gwamnatin Saudiyya ta kwashe wasu ‘yan Najeriya ta cikin teku, domin tsira da rayukansu, kuma da zarar lamarin ya lafa za a yi shirin mayar da su Najeriya.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp