Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa nan ba da wani lokaci ba kadan za ta fara gurfanar da masu daukar nauyin ‘yan ta’adda a fadin kasar nan.
Jaridar The Nation ta rawaito cewa, Ministan Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da manema labarai a ranar Alhamis, 2 ga Febrairu, 2022.
Ya ce, hukumar leken asirin kudade a Najeriya NFIU ce ta gano mutum 96 masu baiwa ‘yan ta’adda kudi, musamman yan Boko Haram da ISWAP.
Ya kara da cewa, NFIU ta bankado mutum 424 dake aiki tare da masu daukar nauyin, kamfanoni 123 da kuma ‘yan kasuwan canji 33.
A cewarsa, “Nan ba da dadewa ba za mu gurfanar da mutum 45 daga cikinsu”. In ji Lai.