Gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya nada Cif Olayide Owolabi Adelami a matsayin mataimakin gwamna a hukumance.
Aiyedatiwa ya zama gwamnan jihar Ondo bayan rasuwar Rotimi Akeredolu.
Akeredolu ya rasu ne a ranar 27 ga Disamba, 2023, a wani asibitin kasar Jamus sakamakon doguwar jinya.