Rahotanni da dumi-dumi na nuni da cewa, wani sashi na babban asibitin yankin Asokoro da ke birnin tarayya Abuja ya kama da wuta.
Sai dai har ya zuwa yanzu ba bu tabbas ko an rasa rai sakamakon gobarar.
Gidan talabijin na Channels cewa, daga bisani an yi nasarar kashe wutan.
Hukumar Kashe Gobara ta Kasa, cikin wani sako da ta wallafa a Twitter ta ce: “Jami’an mu sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a Babban Asibitin Asokoro a Abuja.”