Ghana ta zama ƙasa ta farko daga Afirka da ta kwaso ƴan ƙasarta da suka tsere wa rikicin Ukraine bayan ƙaddamar da yaƙin da Rasha ta yi.
Rukunin farko na ɗalibai ƴan Ghana 17 sun isa filin jirgin sama na Kotoka a Accra a ranar Talata.
Ministan harakokin wajen Ghana tun da farko ya ce ɗalibai 460 ke kan hanyar tsallakawa zuwa Poland da Hungary da Romania da Slovakia da Jamhuriyyar Czech, ƙasashen da ke makwabtaka da Ukraine.
Zuwa yanzu ba a san adadin yawan ƴan Ghana ba da ke Ukraine inda gwamnatin Ghana ke tattaunawa da iyayen ɗaliban domin tantance yawansu
An ƙiyasta cewa sama da ɗaliban Ghana 1,000 ke karatu a Ukraine. In ji BBC,