Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarni hukunta wadanda suka samar tare da shigo da gurbataccen man fetur a kasar nan.
Muhammadu Buhari ya bayar da wannan umarnin ne a wata takarda da ya fitar a ranar Alhamis ta hannun Garba Shehu, babban mai bada shawara na musamman ga shugaban kasan a harkar yada labarai.
Ya ce,”Duk mai hannu a wannan lamarin, dole ne a hukunta shi kan almundahana da kuma shigo da kaya marasa kyau tare da siyarwa”. In ji Buhari.
Muhammadu Buhari ya kuma umarci hukumomin gwamnati da suka dace da su dauka duk matakin da ya yi daidai da dokar kasar nan, wurin tabbatar da an mutunta tare da bai wa jama’a kariya daga masu almundahana a kasuwa da rashin adalci.