Wani dan takarar shugaban kasa a karkashin jamâiyyar Peoples Democratic Party, Nwachukwu Anakwenze ya janye daga takarar shugaban kasa ya baiwa gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike.
Ko da yake kwamitin tantance shugaban kasa karkashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark ya tantance Likitan da Amurka ta horar da shi daga takara.
Anakwenze a cikin sanarwar nasa ya yi gargadin cewa, idan jamâiyyar ta canza doka a tsakiyar wasan, babu wani dan takara nagari da zai samu damar yin takara cikin adalci.
Ya bayyana cewa, ya janye daga takarar ne saboda matakin da jamâiyyar ta dauka na jefa tikitin takarar shugaban kasa a bude duk da kaâidar shiyyar da ke cikin kundin tsarin mulkin jamâiyyar.