Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Oron a majalisar wakilai a birnin tarayya, Nse Ekpenyong, ya mutu, inji rahoton Politics Nigeria.
Oron birni ne na bakin ruwa kuma ƙaramar hukuma a jihar Akwa Ibom.
Ekpenyong, wanda bai nuna alamun rashin lafiya ba, ya rasu ranar Lahadi. Ya kasance ya na da shekaru 58.
Marigayin dai tsohon dan majalisar dokokin jihar Akwa Ibom ne, kuma tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP a jihar Akwa lbom.
Kafin shiga siyasa, ya kasance Manajan Darakta na Based/Investment Trust Co Nigeria Limited, sannan ya zama babban jami’in gudanarwa (CEO) na Brule Integrated Nigeria Limited.
Sakon ta’aziyya da makusanta suka wallafa a shafukan su na sada zumunta kamar:
Francis Otioro ya rubuta a Facebook: “Na yi farin ciki kawai na sami dama don saduwa da ku. A cikin zuciyata, tunanina gareka ya fi mutuwa Ć™arfi, Hon Nse Ekpenyong.
Mattello Felix ya rubuta a kan Facebook: “Abin mamaki! Rt Hon. Menene Ekpenyong?? Labari mai dadi ga mazabar tarayya ta Oron. Ta yi asarar da yawa.”
DrDurable Osung ya rubuta a shafukan sada zumunta: “Wannan babban rashi ne ga Oron Nation. Amma Allah ne masani! Allah Ya Jikansa Ya Saka Masa Rasuwar Nse Ekpenyong. Adieu yayana kuma abokina!”