An yi bukukuwa a jiya bayan masu garkuwa da mutane sun sako wasu dalibai mata uku na Kwalejin Ilimi ta Jihar Kaduna (KSCOE).
Naija News ta fahimci cewa, kwanaki uku da suka gabata ne aka sace ‘yan matan kuma wadanda suka sace su sun nemi a biya su kudi mai yawa.
An bayyana sunayen daliban da aka sace tun da farko, Racheal Edwin, Esther Ishaya, Promise Tanimu, da Beauty Luka, dukkansu a karamar hukumar Jemaa ta jihar.
Da yake zantawa da Aminiya tun farko kan lamarin, Shugaban kungiyar daliban, Kwamared Benjamin Fie ya ce: “Tuni wadanda suka yi garkuwa da su ke neman a biya su makudan kudin fansa domin a sako su. Muna so mu yi amfani da wannan kafa wajen jawo hankalin al’ummar kwalejin da daukacin daliban da su jajirce wajen yin addu’o’i, da makaranta da kuma iyayensu.”