Shugaban kwamitin riko da tsare-tsare na musamman na jam’iyyar APC, kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya rusa kananan kwamitocin babban taron kasa da gwamnan jihar Neja Abubakar Bello, ya kafa a ranar 26 ga Maris.
Buni a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, ya tabbatar wa mambobin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki a jam’iyyar, da ma ‘yan Najeriya baki daya cewa, jam’iyyar da ke mulki ba ta da rikici.
Buni da Sakataren CECPC na kasa, Sanata John Akpanudoedehe, sun sake dawo da shugabancin jam’iyyar a Laraba a matsayin shugaban kwamitin tsare-tsare na babban taron, biyo bayan umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari.
A cikin rusassun kwamitocin da Bello ya kafa a lokacin da ya zama shugaba a makon da ya gabata, sunayen Buni da Akpanudoedehe sun bace a fili.
Tare da sabon ci gaba, ƙananan kwamitocin da Buni ya kafa a baya za su dauki nauyin shirye-shiryen babban taron.
A yanzu dai kwamitin zai kasance karkashin jagorancin, Abdulahi Gasua, yayin da Dare Oketade zai zama Sakatare.