Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai ƙaddamar da sabbin takardun kuɗin ƙasa da aka sake wa fasali ranar Laraba.
Gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Talata a wajen taron kwamitin tsare-tsaren kuɗi.
Mista Emefele ya ce, babban bankin ƙasar ba zai sauya ranar ƙarshe da ya saka na mayar da tsoffin kuɗin zuwa bankunan ƙasar domin sauya su da sabbin takardun kuɗin ba.
Ya ƙara da cewa shugaban zai ƙaddamar da sabbin takardun kuɗin a lokacin taron majalisar zartarwa na ƙasa.