Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan sabuwar dokar zabe a ranar Juma’a, 25 ga watan Fabrairu.
An yi bikin rattaba hannu kan dokar da aka dade a na cece-kuce a kai a zauren majalisar fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila duk sun hallara.
Ci gaban na zuwa ne wata guda, bayan majalisar dokokin kasar ta gabatarwa shugaban kasar da dokar.
Da yake jawabi a taron, shugaban kasar ya bukaci ‘yan majalisar da su hanzarta yin gyara ga sashe na 84 na dokar wanda ya tanadi haramtawa masu rike da mukaman gwamnati jefa kuri’a a zaben shugabannin jam’iyya ko kuma na ‘yan takara, rahoton BBC.