Shugaba Buhari ya rantsar da sabbin kwamishinonin zabe shida a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Taron rantsarwar ya samu halartan shugaban majalisar dattawa, Dr. Ahmad Lawan, kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila da kuma shugaban INEC, Mahmood Yakubu.
Bayan nan Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a ranar Laraba, 23 ga watan Fabrairu.
Kwamishinonin INEC shida da aka rantsar sune, Mallam Mohammed Haruna daga jihar Neja, Misis May Agbamuche-Mbu daga Delta, Ukaegbu Kenneth Nnamdi daga jihar Abia, Manjo Janar A. B Alkali mai ritaya daga Adamawa, Farfesa Rhoda Gumus daga jihar Bayelsa da kuma Mista Sam Olemekun daga jihar Ondo.