Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ki amincewa da kudirin dokar zabe ta 2021.
THISDAY ta rawaito cewa hakan ne a wata wasika da Buhari ya aikewa shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan, cewa halin da a ke ciki a kasar ba zai ba shi damar sanya hannu kan kudirin ba.
Daga cikin wasu dalilan kin amincewa da kudirin, shugaban ya bayar da misali da tsadar gudanar da zaben fidda gwanin kai tsaye da kalubalen tsaro na sa ido kan zaben da take hakkin ‘yan kasa da kuma mayar da kananan jam’iyyun siyasa saniyar ware.
Buhari ya ce, ya samu shawarwari daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da abin ya shafa, sannan kuma ya yi nazari sosai kan kudurin bisa la’akari da abubuwan da ke faruwa a tarayyar Najeriya a halin yanzu.
Shugaban ya kuma ce zai fi kyau a bar kowace jam’iyyar siyasa ta tantance ‘yan takarar zaben ta.