Gwamnatin tarayya ta cika alkawarin da ta dauka na bayar da gidaje ga wadanda suka lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekarar 1994.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a ranar Litinin, a wajen kaddamar da ayyukan gina gidaje a karkashin shirin NHP na mataki na daya a Abere, jihar Osun, ya ce, ‘yan wasan za su iya karbar makullan gidajensu a jihohin da suke so.
Shugaban wanda ya samu wakilcin ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya bayyana cewa, manufar gwamnatin tarayya ya wuce inganta rayuwar bil’adama ta hanyar ayyukan gidaje, amma kuma ta na ba da damar cika alkawarin da ta dauka.