fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Buhari ya amince da dala miliyan 8.5 a fara kwaso ‘yan Najeriya daga Ukraine

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da bayar da dala miliyan 8.5 ga ma’aikatun harkokin kasashen waje da ayyukan jin kai, magance bala’o’i, da ci gaban jama’a, domin kwashe ‘yan Najeriya sama da 5,000 (masu rijista da marasa rijista) da ke makale a kasar Ukraine.

Karamin Ministan Harkokin Waje, Zubairu Dada ne ya bayyana hakan a ranar Laraba.

Ministan ya shaidawa manema labarai na fadar gwamnati, bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya cewa, za a aike da jiragen sama guda uku zuwa kasashe hudu.

A cewarsa, kasashen da za a fara jigilar jiragen sun hada da Poland, Hungary, Slovakia, da Romania.

Ana sa ran jiragen biyu daga Air Peace da kuma na Max Air za su gudanar da aikin kwashe mutanen.

Dada ya ce, dukkan hukumomin sun ba da cikakken kayan aiki, domin tabbatar da cewa jiragen sun tashi a ranar Laraba domin fara kwashe su. Sun yi nuni da cewa, jiragen za su yi tafiya da yawa har sai an kammala aiki.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp