Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da bayar da dala miliyan 8.5 ga ma’aikatun harkokin kasashen waje da ayyukan jin kai, magance bala’o’i, da ci gaban jama’a, domin kwashe ‘yan Najeriya sama da 5,000 (masu rijista da marasa rijista) da ke makale a kasar Ukraine.
Karamin Ministan Harkokin Waje, Zubairu Dada ne ya bayyana hakan a ranar Laraba.
Ministan ya shaidawa manema labarai na fadar gwamnati, bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya cewa, za a aike da jiragen sama guda uku zuwa kasashe hudu.
A cewarsa, kasashen da za a fara jigilar jiragen sun hada da Poland, Hungary, Slovakia, da Romania.
Ana sa ran jiragen biyu daga Air Peace da kuma na Max Air za su gudanar da aikin kwashe mutanen.
Dada ya ce, dukkan hukumomin sun ba da cikakken kayan aiki, domin tabbatar da cewa jiragen sun tashi a ranar Laraba domin fara kwashe su. Sun yi nuni da cewa, jiragen za su yi tafiya da yawa har sai an kammala aiki.