fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Boko Haram sun kashe ‘yan gwangwan 55 a Borno

Date:

Akalla masu sana’ar tattara karafa wato ‘yan gwangwan 55 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare da mayakan Boko Haram suka hada kai a cikin makonni uku da suka gabata a Borno.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abdu Umar ne ya bayyana haka yayin da yake magana a gefen taron masu ruwa da tsaki na tsaro a ranar Asabar a Maiduguri.

Masu ruwa da tsakin sun hada da ‘yan sanda, Sojoji, Tsaron Najeriya da Civil Defence (NSCDC), da kuma DSS da dai sauransu.
Taron dai an yi shi ne domin tattaunawa tare da samar da mafita kan hare-haren da ake kaiwa masu tarin karafa a jihar.

Umar ya ce, ‘yan ta’addan sun kashe masu tarin karafa 32 a kauyen Modu da ke karamar hukumar Kala-Balge yayin da wasu 23 suka kashe a kauyen Mukdala na karamar hukumar Dikwa.

Ya ce wadanda lamarin ya rutsa da su sun kutsa cikin dazuzzukan da ke da tazarar kilomita 25 daga garuruwan ba tare da sanar da jami’an tsaro tattara karafa ba.

Ya ce, Gwamna Babagana Zulum ya umurci hukumomin tsaro da su dauki matakan dakile kashe-kashen, domin dakile afkuwar lamarin nan gaba.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp