fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Boko Haram sun kashe ‘yan gwangwan 55 a Borno

Date:

Akalla masu sana’ar tattara karafa wato ‘yan gwangwan 55 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare da mayakan Boko Haram suka hada kai a cikin makonni uku da suka gabata a Borno.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abdu Umar ne ya bayyana haka yayin da yake magana a gefen taron masu ruwa da tsaki na tsaro a ranar Asabar a Maiduguri.

Masu ruwa da tsakin sun hada da ‘yan sanda, Sojoji, Tsaron Najeriya da Civil Defence (NSCDC), da kuma DSS da dai sauransu.
Taron dai an yi shi ne domin tattaunawa tare da samar da mafita kan hare-haren da ake kaiwa masu tarin karafa a jihar.

Umar ya ce, ‘yan ta’addan sun kashe masu tarin karafa 32 a kauyen Modu da ke karamar hukumar Kala-Balge yayin da wasu 23 suka kashe a kauyen Mukdala na karamar hukumar Dikwa.

Ya ce wadanda lamarin ya rutsa da su sun kutsa cikin dazuzzukan da ke da tazarar kilomita 25 daga garuruwan ba tare da sanar da jami’an tsaro tattara karafa ba.

Ya ce, Gwamna Babagana Zulum ya umurci hukumomin tsaro da su dauki matakan dakile kashe-kashen, domin dakile afkuwar lamarin nan gaba.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp