‘Yan ta’addan Boko Haram da ke samun goyon bayan kungiyar Da’ish, Lardin Islamic State West Africa da ake kira Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, suna kai farmaki a kauyen Kautikari da ke karamar hukumar Chibok a Jihar Borno.
SaharaReporters ta tattaro cewa, ‘yan ta’addan sun mamaye garin ne a ranar Talata, inda suka rika harbe-harbe a kai a kai yayin da mazauna unguwar suka tsere zuwa cikin dajin domin tsira da rayukansu.
Sojojin da aka ajiye a sansanin sojojin gaba (FOB) da ke Kada mai tazarar kilomita 2 daga Kautukari, suma maharan sun tarwatsa su.
“An kai wa al’umma hari, wannan shi ne hari na hudu a bana kadai, don Allah a yi mana addu’a,” kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa SaharaReporters.
A watan Disamba 2021 da Janairu 2022, Kautikari ya fuskanci hare-hare daga masu tayar da kayar baya wadanda suka sace mata da yara da dama.
Har ila yau, maharan sun yi wa wata majami’a a yankin wuta a yayin hare-haren.
Hare-haren da aka kai a yankunan Chibok, musamman wanda ya faru a watan Janairun 2022, ya sanya gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ziyarci yankin domin karfafa gwiwar jama’a da kuma jami’an tsaro da aka jibge a karamar hukumar.
A yayin ziyarar gwamnan ya gana da iyalan mata 22 da maza biyu da maharan suka yi garkuwa da su inda ya bukaci su ci gaba da dogara ga Allah ta hanyar addu’a.