Wata babbar mota ta murkushe motoci hudu a ranar Lahadi a Abuja, kusa da gadar Karu da babbar hanyar Abuja zuwa Nyanya Keffi mai cunkoso.
Rohtanni sun ce hatsarin da ya afku ya haifar da cunkoson munanan ababen hawa a kan hanyar.
Jami’an kiyaye haddura na tarayya da na rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Karu sun isa wurin da hatsarin ya faru cikin gaggawa inda suka nufi hanyar ajiye motoci.
Sai dai kwamandan sashin babban birnin tarayya, FRSC, Mista Samuel Ogar Ochi, ya mayar da martani kan lamarin inda ya bayyana cew,a babu wanda ya jikkata kuma hatsarin ya faru ne da misalin karfe 9:30 na safe.
A cewarsa, “Wadanda suka samu raunuka an garzaya da su asibiti domin yi musu magani.
” Kwamandan runduna ta FRSC da wasu jami’an mu suna wurin da hadarin ya afku. A gaskiya babbar motar mu tana kan hanya don kwashe baraguzan kan hanya amma babu wanda ya mutu.
” Za su share hanyar, sun karkatar da ababen hawa daga babban titin zuwa titin ajiye motoci. Hukumar bada agajin gaggawa ta FRSC ta kwashe wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Asokoro dake Abuja domin yi musu magani.”