Ɗan takarar shugaban kasa ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya jagoranci wata zanga-zangar lumana da jam’iyyarsa ta shirya a Abuja domin nuna adawa da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar na 2023.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa Iyorchia Ayu, da ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta, da kuma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal na daga cikin waɗanda suka halarci zanga-zangar.
Ita dai jam’iyyar PDP na zargin an tafka maguɗi a zaɓen wanda ya gudana a ranar 23 ga watan Fabarairu, wanda hukumar zaɓen Najeriya -INEC ta sanar da ɗan takarar APC mai mulki, Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen.