Jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da ranar da za ta gudanar babban taron ta na kasa.
Jaridar Blueprint ta rawaito cewa a na sa ran, babban taronta na kasa zai wakana ne a tsakanin ranakun 25 zuwa 26 ga watan Fabrairu.
Da ya ke tabbatar da ranar a wannan Juma’ar ga jaridar ta Blueprint a Abuja, wani jigo a jam’iyyar, wanda ya nemi a sakaye sunansa ya ce kwamitin riko na musamman a karkashin Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya amince da gudanar da taron a tsakanin ranakun 25 zuwa 26 ga watan Fabrairu.
Ya ce “Zan iya gaya muku cewa, za a gudanar da babban taron mu na kasa nan da ranar 25 ko 26 ga watan Fabrairu a nan Abuja, wanda kwamitin riko na kasa ya tabbatar”.