fidelitybank

Da Dumi-Dumi: APC ta kori masu neman tsayawa takarar shugaban kasa su 10

Date:

Kwamitin tantancewar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya kori mutane 10 da suka tsaya takarar shugabancin jam’iyyar.

Shugaban kwamitin, John Odigeie-Oyegun ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake mika rahotonsa ga shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Adamu.

Sai dai bai bayyana sunayen wadanda aka soke ba.

Kwamitin ya tantance ‘yan takarar shugaban kasa 23 a ranakun Litinin da Talata.

Wadanda aka tantance sun hada da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu; wani malami, Tunde Bakare; Gwamna Abubakar Badaru na Jigawa; tsohon gwamnan Ogun, Ibikunle Amosun; tsohon gwamnan Zamfara, Sani Yerima da Rotimi Amaechi, tsohon ministan sufuri.

Sauran sun hada da tsohon karamin ministan ilimi, Emeka Nwajiuba; Felix Nicholas, fasto; mace daya tilo da ta tsaya takarar shugaban kasa, Uju Ken-Ohanenye; dan majalisar dattawa, Ajayi Boroffice; tsohon shugaban majalisar dattawa, Ken Nnamani da gwamna David Umahi na jihar Ebonyi. In ji Premium Times.

Gwamnan jihar Cross Rivers, Ben Ayade; Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan; Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi; Tein Jack-Rich; tsohon ministan kimiyya da fasaha, Ogbonnaya Onu; tsohon ministan yada labarai, Ikeobasi Mokelu; tsohon kakakin majalisar wakilai, Dimeji Bankole; Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi; Haka kuma an tantance tsohon ministan harkokin Neja Delta Godswill Akpabio da tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp