fidelitybank

Da Dumi-Dumi: APC ta kori masu neman tsayawa takarar shugaban kasa su 10

Date:

Kwamitin tantancewar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya kori mutane 10 da suka tsaya takarar shugabancin jam’iyyar.

Shugaban kwamitin, John Odigeie-Oyegun ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake mika rahotonsa ga shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Adamu.

Sai dai bai bayyana sunayen wadanda aka soke ba.

Kwamitin ya tantance ‘yan takarar shugaban kasa 23 a ranakun Litinin da Talata.

Wadanda aka tantance sun hada da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu; wani malami, Tunde Bakare; Gwamna Abubakar Badaru na Jigawa; tsohon gwamnan Ogun, Ibikunle Amosun; tsohon gwamnan Zamfara, Sani Yerima da Rotimi Amaechi, tsohon ministan sufuri.

Sauran sun hada da tsohon karamin ministan ilimi, Emeka Nwajiuba; Felix Nicholas, fasto; mace daya tilo da ta tsaya takarar shugaban kasa, Uju Ken-Ohanenye; dan majalisar dattawa, Ajayi Boroffice; tsohon shugaban majalisar dattawa, Ken Nnamani da gwamna David Umahi na jihar Ebonyi. In ji Premium Times.

Gwamnan jihar Cross Rivers, Ben Ayade; Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan; Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi; Tein Jack-Rich; tsohon ministan kimiyya da fasaha, Ogbonnaya Onu; tsohon ministan yada labarai, Ikeobasi Mokelu; tsohon kakakin majalisar wakilai, Dimeji Bankole; Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi; Haka kuma an tantance tsohon ministan harkokin Neja Delta Godswill Akpabio da tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp