Rahotanni na cewa masu garkuwa da mutane sun sace mutane da dama a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a ranar Talata.
Wani wanda ya shaida lamarin ya bayyana wa BBC cewa, lamarin ya faru ne a garin Katari da misalin 4:30 na yammaci.
Ya bayyana cewa akwai motoci da dama waɗanda suna ajiye a kan ɓangaren zuwa Kaduna da ɓangaren dawowa da aka yi awon gaba da masu motocin.
Ya kuma ce bayan faruwar lamarin jami’an tsaro masu É—umbin yawa sun isa wurin domin kai É—auki.
BBC ta tuntuɓi gwamnatin Jihar Kaduna da kuma rundunar ƴan sadan Najeriya reshen Kaduna domin jin ƙarin bayani, sai dai dukansu ba su ɗaga wayoyinmu ba