fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An yi garkuwa da matar shugaban ma’aikatan NULGE a Zamfara

Date:

An yi garkuwa da matar shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin jihar Zamfara, Sanusi Mohammed Gusau.

Matar mai suna Ramatu Yunusa, an sace ta ne daga gidan mijinta da ke Damba Gusau da safiyar Talata.

Gusau wanda ya bayyana hakan ga jaridar The Punch, ya ce ‘yan bindigar sun shiga gidansa da misalin karfe daya na safiyar ranar Talata, inda suka yi awon gaba da matarsa mai ciki wadda za a haifo jaririn a kowane lokaci.

A cewarsa, yana farkawa ne a lokacin da ‘yan fashin suka tsallake shingen da nufin sace shi amma kwatsam ya buya inda ba su gan shi ba.

Gusau ya ce, “Sun tsallake bango suka karya min kofa amma kafin su shiga dakina na buya a wani wuri.

“Lokacin da suka binciki gidan ba su gan ni ba, sai suka sace matata mai ciki, Ramatu.”

“Tana iya haihuwa kowane lokaci daga yanzu saboda ranar da ake sa ran haihuwa a cikin wannan makon.”

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu ‘yan bindigar ba su kai gare shi ba.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp