fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An yi garkuwa da daliban jami’ar tarayya ta Nasarawa

Date:

An yi garkuwa da wasu daliban jami’ar tarayya dake garin Lafia a jihar Nasarawa a kusa da harabar jami’ar.

Majiyar Daily Trust ta rwaito cewa, Majiyarmu ta bayyana cewa, an sace daliban ne a unguwar jami’ar da ke Maraba.

Jami’in hulda da jama’a na jami’ar, Abubakar Ibrahim ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an sace dalibai hudu.

Ya ce, ‘yan bindigar sun far wa jama’ar jami’ar ne da misalin karfe 11:30 na ranar Alhamis inda su ka garzaya da daliban zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

“Mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Shehu Abdul Rahman, a madadin shugabannin hukumar, ya nuna matukar bacin ransa game da wannan abin takaici, ya kuma yi Allah wadai da shi da kakkausar murya da bukatar a gaggauta sakin wadanda aka sace.”

An jiyo mataimakin shugaban jami’ar na cewa, sace dalibai ya kasance daya daga cikin munanan matsalolin da ke barazana ga ilimi a jihar Nasarawa, musamman ma Najeriya baki daya.

Yayin da ya ke jajantawa iyalan daliban da aka sace, ya kuma tabbatar musu da cewa a na kokarin ganin an ceto wadanda lamarin ya shafa cikin gaggawa.

Sanarwar ta kara da cewa, “Mataimakin shugaban jami’ar, wanda tun lokacin da ya ziyarci yankin da aka yi garkuwa da daliban, ya ziyarci rundunar ‘yan sandan Nasarawa inda ya sanar da kwamishinan ‘yan sanda game da sace daliban.”

Rahotanni sun bayyana cewa, Farfesa Rahman ya bukaci daliban da su kara mai da hankali kan al’amuran da suka shafi tsaro, ya kuma yi kira gare su da su kwantar da hankalinsu su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Ya yi nuni da cewa, an samar da karin matakan tabbatar da isassun tsaron rayuka da dukiyoyi a ciki da wajen Jami’ar.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp