An yi garkuwa da wasu daliban jami’ar tarayya dake garin Lafia a jihar Nasarawa a kusa da harabar jami’ar.
Majiyar Daily Trust ta rwaito cewa, Majiyarmu ta bayyana cewa, an sace daliban ne a unguwar jami’ar da ke Maraba.
Jami’in hulda da jama’a na jami’ar, Abubakar Ibrahim ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an sace dalibai hudu.
Ya ce, ‘yan bindigar sun far wa jama’ar jami’ar ne da misalin karfe 11:30 na ranar Alhamis inda su ka garzaya da daliban zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.
“Mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Shehu Abdul Rahman, a madadin shugabannin hukumar, ya nuna matukar bacin ransa game da wannan abin takaici, ya kuma yi Allah wadai da shi da kakkausar murya da bukatar a gaggauta sakin wadanda aka sace.”
An jiyo mataimakin shugaban jami’ar na cewa, sace dalibai ya kasance daya daga cikin munanan matsalolin da ke barazana ga ilimi a jihar Nasarawa, musamman ma Najeriya baki daya.
Yayin da ya ke jajantawa iyalan daliban da aka sace, ya kuma tabbatar musu da cewa a na kokarin ganin an ceto wadanda lamarin ya shafa cikin gaggawa.
Sanarwar ta kara da cewa, “Mataimakin shugaban jami’ar, wanda tun lokacin da ya ziyarci yankin da aka yi garkuwa da daliban, ya ziyarci rundunar ‘yan sandan Nasarawa inda ya sanar da kwamishinan ‘yan sanda game da sace daliban.”
Rahotanni sun bayyana cewa, Farfesa Rahman ya bukaci daliban da su kara mai da hankali kan al’amuran da suka shafi tsaro, ya kuma yi kira gare su da su kwantar da hankalinsu su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum.
Ya yi nuni da cewa, an samar da karin matakan tabbatar da isassun tsaron rayuka da dukiyoyi a ciki da wajen Jami’ar.