An rantsar da Abiodun Oyebanji na jamâiyyar All Progressives Congress, APC a matsayin gwamnan jihar Ekiti.
Oyebanji ya yi rantsuwar kama aiki a gidan gwamnatin jihar ranar Lahadi da misalin karfe 12:53 na rana.
Babban alkalin jihar, Justice Oyewole Adeyeye ne ya rantsar da tsohon sakataren gwamnatin jihar, SSG.
Manyan mutanen da suka halarci taron sun hada da dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar APC, Bola Tinubu; Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu da takwaransa na jihar Filato, Simon Lalong.
Sauran sun hada da Gwamna Babajide Sanwo-Olu (Lagos), Godwin Obaseki (Edo), Abubakar Badaru (Jigawa), Dapo Abiodun (Ogun) da dai sauransu.
An ayyana Oyebanji a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Ekiti bayan ya samu kuriâu 187,057.
Ya doke abokan hamayyarsa guda biyu – Segun Oni na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) wanda ya samu kuri’u 82,211, da Bisi Kolawole na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), wanda ya samu kuri’u 67,457.