fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An kumasace mutane fiye da 80 a Kaduna

Date:

Rahotanni na daga jihar Kaduna na cewa, wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutum fiye da 80 a garin Kajuru a wani sabon hari da suka kai garin ranar Lahadi.

Harwayau, ‘yan bindigar sun fasa shaguna inda suka saci kayan abinci da sauran muhimman kayayyaki kamar yadda wani shaida ya fada wa BBC.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mansur Hassan ya tabbatar da sace mutanen ga BBC sai dai bai fadi yawan adadin da kafafen watsa labarai ke ambatawa ba.

Hassan ya ce nan ba da jimawa ba za su sanarwa da manema labarai da jama’a iya adadin mutanen da aka sace kasancewar har yanzu ana tantancewa.

“Eh, gaskiya mun samu wannan labari na masu garkuwa da mutane sun sake sace mutane da dama, amma har yanzu ba a san iya adadin mutanen da aka sace ba saboda daji ne gurin.” in ji Hassan

“Shiyasa kullum muke kira ga jama’a da cewa duk lokacin da suka ga gittawar waÉ—annan mutanen, ba sai laile sun kai hari ba, a yi Æ™oÆ™ari a sanar da mu saboda irin waÉ—annen wurare daji ne sosai”

“Saboda kusan yaÆ™in da ake yi da waÉ—annan Æ´an ta’adda da kusan jama’an gari ake yi.

Hassan ya ce rundunar jihar ta tura Æ™arin jami’an tsaro don bin sawun mutanen da aka Æ™ara sacewa.

Harin dai na zuwa ne ƙasa da kwana biyu bayan an sace wasu mata fiya mata 15 tare da wani namiji ɗaya a ƙauyen Dogon Nama duk dai a ƙaramar hukumar ta Kajuru.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp