Hukumar ƴan sanda a jihar Kano, ta tabbatar da cewa an cinna wa ofishin hukumar zaɓe ta ƙasar reshen ƙaramar hukumar Takai wuta.
Kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna kiyawa ne ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin.
‘Ƴan banga ne suka cinna wa janareton da ake aiki da shi a cibyar wuta, lokacin da suka shiga wajen ta baya, amma ba wani ci ta yi ba, kuma an kashe ta, tuni muka ƙara yawan jami’anmu a wajen,’ in ji Kiyawa.
Karanta Wannan: Zamu fara faɗan sakamakon zaɓe da tsakar ranar yau – INEC
BBC ta tuntuɓi wani ganau wanda ya ce an cinna wutar kuma ta ƙona wasu robobi da aka zuba takardun ƙuri’un da aka ƙada amma ba ta ƙona wajen da ake aikin ƙirga ƙuri’u ba.