Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani malamin makaranta tare da wasu mutane hudu a hanyar Layin Lasan Tabanni a karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.
Rahotannin sun bayyana cewa an kuma yi garkuwa da mutane 16 a kauyukan Dogon Dawa, Layin Mahuta da Tabanni dake Gabashin karamar hukumar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Birnin Gwari Vanguard ya fitar mai kula da harkokin tsaro da kyakkyawan shugabanci mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar,
A cewarsu, a ranar 14 ga Maris, wasu ‘yan bindiga sun kashe Haruna Tanko Dogon Dawa da wasu biyu a hanyar Dogon Dawa zuwa Zariya.
“An yi garkuwa da wasu mutane takwas a hanya daya. A Layin Mahuta (Tabanni) an kashe wani Abdullahi Abubakar malamin makaranta a kan hanyar Layin Lasan Tabanni ranar Laraba 16 ga Maris 2022. Yayin da a ranar Alhamis 17 ga wata, an kuma kashe wata tsohuwa mai shekaru 70 tare da sace mata bakwai a Layin Mahuta Tabanni. An sace wasu mutane biyu a tsohon Tabanni,” Ibrahim Abubakar Nagwari.”
Shugaban ya kara da cewa a yankin Randagi ‘yan bindiga sun sako mutane 32 daga cikin 46 da aka yi garkuwa da su a Unguwar Bula da Ijinga makonni uku da suka gabata bayan sun biya Naira miliyan 16 kudin fansa.
Kungiyar ta kuma bukaci jami’an tsaro da su rika amsa kiraye-kirayen kai daukin gaggawa a unguwannin Dogon Dawa, Kuyello, Tabanni, da Kutemashi a cikin Birnin Gwari.