fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An kashe Malamin makaranta tare da yin garkuwa da mutane 16 a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani malamin makaranta tare da wasu mutane hudu a hanyar Layin Lasan Tabanni a karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna.

Rahotannin sun bayyana cewa an kuma yi garkuwa da mutane 16 a kauyukan Dogon Dawa, Layin Mahuta da Tabanni dake Gabashin karamar hukumar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Birnin Gwari Vanguard ya fitar mai kula da harkokin tsaro da kyakkyawan shugabanci mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar,

A cewarsu, a ranar 14 ga Maris, wasu ‘yan bindiga sun kashe Haruna Tanko Dogon Dawa da wasu biyu a hanyar Dogon Dawa zuwa Zariya.

“An yi garkuwa da wasu mutane takwas a hanya daya. A Layin Mahuta (Tabanni) an kashe wani Abdullahi Abubakar malamin makaranta a kan hanyar Layin Lasan Tabanni ranar Laraba 16 ga Maris 2022. Yayin da a ranar Alhamis 17 ga wata, an kuma kashe wata tsohuwa mai shekaru 70 tare da sace mata bakwai a Layin Mahuta Tabanni. An sace wasu mutane biyu a tsohon Tabanni,” Ibrahim Abubakar Nagwari.”

Shugaban ya kara da cewa a yankin Randagi ‘yan bindiga sun sako mutane 32 daga cikin 46 da aka yi garkuwa da su a Unguwar Bula da Ijinga makonni uku da suka gabata bayan sun biya Naira miliyan 16 kudin fansa.

Kungiyar ta kuma bukaci jami’an tsaro da su rika amsa kiraye-kirayen kai daukin gaggawa a unguwannin Dogon Dawa, Kuyello, Tabanni, da Kutemashi a cikin Birnin Gwari.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp