fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An kama wanda ake zargi da kashe Ahmed Gulak

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta sanar da kama daya daga cikin wadanda ake zargi da kashe Ahmed Gulak, tsohon mai baiwa shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Imo, Mike Abattam, yayin da yake gabatar da wanda ake zargin, Chimobi Anosike, ya bayyana cewa, an kama shi ne bayan wani dogon bincike da jami’an tsaro suka gudanar.

Politics Nigeria ta rawaito cewa, an kashe Gulak ne cikin ruwan sanyi a ranar 30 ga Mayu, 2021 akan hanyarsa ta zuwa filin jirgin saman Sam Mbakwe International Cargo a Owerri.

Da yake gabatar da wanda ake zargin, Anosike Chimobi mai shekaru 38, daga Umuedo, a karamar hukumar Ahiazu Mbaise a jihar, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Micheal Abattam, ya bayyana cewa an kama Chimaobi ne biyo bayan wani dogon bincike da jami’an rundunar suka gudanar.

Abattam ya bayyana cewa; “Yan ta’addan da suka kashe Ahmed Gulak a ranar 30 ga Mayu, 2021, a kan titin filin jirgin sama na jihar Imo. Da yake da hannu wajen kona Aboh Mbaise, Ahiazu Mbaise, Ezinihitte Mbaise, Ihitte-Uboma, da kuma ofisoshin ‘yan sanda na Obowo, ya bayyana cewa yana cikin ‘yan ta’addan da suka kai wa motar albasa hari a mahadar Enyiogwugwu mahadar Aboh Mbaise, jihar Imo, a ranar 30 ga watan Mayu. ”

“Ya amsa laifinsa da hannu wajen kai hari da kashe jami’an ‘yan sanda da dama da kuma tarin bindigu na hidima. Ya kuma amsa laifin yin garkuwa da wani Jude Nwahiri a Eke Nguru Junction Aboh Mbaise L.G.A, Jihar Imo, a karkashin wani kwamandan Ebube Uche Madu aka virus, wanda ke cikin jerin sunayen ‘yan sandan da ake nema ruwa a jallo.”

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...
X whatsapp