fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An hrabe Baturen ‘yan sandan Neja da mutane hudu

Date:

A ranar Lahadi ne wasu ‘yan bindiga suka kashe DPO, Mukhtar Sabiu da wasu mutane hudu a garin Paiko, hedikwatar karamar hukumar Paikoro ta jihar Neja.

Wani mazaunin yankin mai suna Musa Idris wanda ya ce da kyar ya tsere, ya ce an harbe wadanda aka kashen ne a kauyen Kwakuti da ke kan hanyar Minna zuwa Suleja ranar Asabar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya ce an kashe DPO da mutanen sa ne a wani artabu da bindiga.

Ya ce rundunar ta samu bayanai da misalin karfe 1100 na sa’o’i, cewa an ga ‘yan bindiga dauke da makamai a kusa da kauyukan Kwakuti-Dajigbe na Lambata, a kokarinsu na kai farmaki kan wasu al’ummomin da ke kusa da karamar hukumar Gurara.

Hedikwatar ‘yan sanda ta kasa ta tattara tawagar jami’ai da maza daga Dibishin Gawu-Babangida da na Paiko; An kuma shirya jami’an soji da na ‘yan banga zuwa wurin.

Ya ce ‘yan sandan sun yi musu artabu da bindiga tare da dakile harin inda aka kashe da dama daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp