Gwamnatin tarayya ta dage kashin farko na ‘yan Najeriya da ake sa ran za su dawo daga kasar Ukraine ranar Alhamis.
A cewar wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen kasar nan, Bolaji Akinremi, cewa an dage tashin jirgin ne saboda tsaikon da aka samu na shirya fasinjojin da za a shiga.
Yanzu haka jirgin na Air Peace zai iso Najeriya da safiyar Juma’a. A cewar sanarwar.
Hakan na nufin ‘yan Najeriya mazauna kasar Ukraine na kasashen Hungary, Poland, Romania da Slovakia wanda wasua za su kara zuwa kasashen a ranar Alhamis.
Idan za a iya tunawa a ranar Laraba, ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta sanar da cewa, ta na sa ran za ta karbi kashin farko na ‘yan Najeriya daga Ukraine a ranar Alhamis.