Labari da muke samu a yanzu haka cewa, Allah ya yiwa mataimakin shugaban Kwalejin Ilimi ta Tarayya ta Katsina, (FCE), Dr. Ibrahim Abubakar Gafai, rasuwa.
A cewar wata majiya ta iyalansa, Dr. Gafai ya rasu ne a yau Alhamis, 10 ga watan Fabrairu, bayan ya yi fama da dogon jinya.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, yanzu haka a na shirye-shiryen gudanar da jana’izarsa a gidansa da ke Quarters din Gafai, bayan gidan man AP.