fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Abubakar Bello ya dakatar da hakar ma’adanai a Neja

Date:

Gwamnan Jihar Neja Abubakar Sani Bello, ya sanar da dakatar da haƙar ma’adinai a Ƙananan Hukumomin Shiroro da Munya da Rafi.

Gwamnan ya bayyana haka ne biyo bayan harin da ƴan bindiga suka kai wani wurin haƙar ma’adinai da ke ƙauyen Ajata Aboki da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke jihar.

A cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Ahmed Ibrahim Matane ya fitar, sakataren ya ce akwai buƙatar a dakatar da haƙar ma’adinai sakamakon yadda rashin tsaro ke ƙara ƙamari ƴan kwanakin nan.

Ya ce sun lura da cewa wuraren haƙar ma’adinan na jawo masu aikata laifuka waɗanda suke kasancewa barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a.

Ya kuma yi gargaɗin cewa duk waɗanda aka kama suna gudanar da ayyukan haƙar ma’adinai za su yaba wa aya zaƙinta

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp