fidelitybank

Da Dumi-Dumi: A na zanga-zanga a Sokoto

Date:

Zanga-zanga ta ɓarke a garin Sokoto, inda matasa ke ci gaba da nuna ɓacin ransu kan kalaman ɓatanci da ya jawo kisan wata matashiyar ɗaliba mai suna Deborah Samuel.

Masu zanga-zangar na neman jami’an tsaro su saki mutanen da suka kama da ake zargi da kisan matashiyar da ke karatu a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari, wadda suka zarga da zagin Annabi Muhammadu (SWA).

Matasan maza da mata suna aiwtar da zanga-zangar a wurare daban-daban a fadin Sokoto tare da ƙona tayoyi, da suka haɗa da Fadar Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III. Kazalika wasu sun yi cincirundo a ƙofar gidan gwamnatin jihar.

Rahotannin da BBC ta samu sun nuna cewa da farko zanga-zangar ta lumana ce, daga bisani sai ta rikide ta zuwa tamkar rikici, inda mutane suka dinga jefa duwatsu kan gidan sarkin Musulmin.

Wani da BBC ta zanta da shi da ke kusa da fadar sarkin a lokacin da abin ya faru ya ce jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin dakatar da matasan kutsawa fadar.

“Da yawa yaran (‘yan zanga-zanga) na ganin sarkin ya goyi bayan yarinyar (Deborah), shi ne suke jefe-jefe,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro na ‘yan sanda da soja sun harba hayaƙi mai sa hawaye, har ma an harbi mutum biyu.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp