Majiyoyin daga cikin jam’iyyar APC sun bayyana cewa, a na shirin dage taron gangaminta na kasa da a ka shirya gudanarwa a cikin watan Fabrairu.
A cewar majiyoyin, za a gabatarwa shugaba Buhari wannan shawara idan ya dawo Najeriya daga Brussels.
Da alamun taron gangamin jam’iyyar APC da a ka shirya yi ranar 26 ga Febrairu, 2022, ba zai yiwu ba.
A cewar rahoton ThisDay, a na shirin dage taron gangamin da makonni biyu.