Rahotannin da ke nuni da cewa mayakan ISAWP sun tashi bama-bamai a Maiduguri babban birnin jihar Borno a wurare da dama.
Lamarin na faruwa ne a yayin da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai isa birnin domin ziyarar aiki.
Masu iƙirarin jihadi sun harba makamai cikin Maiduguri, kamar yadda wasu bayanai su ka nuna cewa kusan bama-bamai Tara a ka harba a Bulunkutu da Ngomari da kuma Ayafe da ke kusa da filin jirgin saman birnin.
Wani mazaunin birnin, Adamu Aliyu Ngule, ya shaida wa BBC cewa rokokin da a ka harba sun lalata wasu gidaje da ke kusa da filin jirgin sama.
A cewarsa “Mutum hudu sun rasu biyu kuma su na samun kulawar likitoci a asibiti, al’ummar unguwar sun fada halin alhini a yayin da a ke murnar ziyarar da shugaban kasa zai kawo”. Inji Adamu.
Hukumomi a jihar ta Borno sun tabbatar wa BBC Hausa aukuwar lamarin sai dai ba su yi karin bayani kan ta’adin da bama-baman su ka yi ba kawo yanzu.