Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinsbajo, ya ce, jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin kasar har yanzu ta na daya daga cikin jihohin da suka fi samun sa’a a kasar, sakamakon shugabancin da ta yi cikin shekaru 11 da suka gabata.
Ya kuma bayyana cewa, shugabanci ba wai rike mukamai masu daraja ba ne kawai, amma sadaukarwa da yi wa jama’a hidima.
Osinbajo ya bayyana haka ne a daren ranar Litinin a Abuja, a wajen bikin cika shekaru biyar da kafa cibiyar horas da yara ta Arewa maso Gabas; Cibiyar koyar da ayyukan jin kai da ya zayyana a shekarar 2016 kuma ta fara aiki bayan shekara guda a Maiduguri, ga yaran marayu da ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas.
Babban mataimaki na musamman ga mataimakin shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Laolu Akande, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Talata mai taken Shugabanci na gaskiya ya shafi yi wa mutane hidima, Osinbajo ya ce, a yayin da yaran Arewa maso gabas ke cika shekaru biyar.
A cewarsa, “Na yi imanin cewa, jihar Borno na iya kasancewa daya daga cikin jihohin da suka fi samun sa’a a kasar nan, kawai ta hanyar shugabancin da jihar ta samu. Nan da nan bayan Gwamna Shettima, Gwamna Zulum ya zo.
“Babu wata jiha da za ta iya neman abin da ya fi Gwamna Zulum, wanda ya karbi mulki daga hannun magabacinsa, Gov Shettima.”
Ya yabawa Gwamnonin Jihar Borno da suka dade da kuma na yanzu: Kashim Shettima da Babagana Zulum bisa rawar da suka taka wajen bunkasa Cibiyar inda ya ce “idan ba za ku iya yi wa jama’a hidima da duk wani abu da kuke da shi da kuma dukkan zuciyarku ba, to ta haka ne, zai zama mara amfani kuma watakila ma rashin hakki”.