Gwamna Bala Mohammed ya ce da jam’iyyar PDP ta baiwa jagoran jam’iyyar APC na kasa Bola Tinubu tikitin takarar shugaban kasa idan yana PDP.
Bala, a wata hira da ya yi da Arise News, ya ce jam’iyyar PDP ta amince da gudunmawar da Tinubu ya bayar wajen ci gaban kasa da kuma goyon bayan Shugaba Muhammadu Buhari.
“Na hadu da Asiwaju Bola Tinubu. Mun tattauna. Yana magana ne a kan yarjejeniya, sai na ce masa, da a ce kana PDP, da mun ba ka tikitin takara ne, domin mun san cewa in ba kai ba, da Buhari ba zai zama shugaban kasa ba, kuma a PDP mun amince da gudunmawar. ,” ya bayyana.
Kalaman gwamnan Bauchi ya zo ne a daidai lokacin da ake ta rade-radin cewa tasirin Mista Tinubu ba zai isa ya samu tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ba.
A makon da ya gabata, Gwamna Nyesom Wike, mai fatan zama shugaban kasa a PDP, ya ce duk masu neman shugabancin jam’iyyar APC, ciki har da Mista Tinubu, sun fi Buhari sharri.