fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Zaɓaɓen ɗan majalisar wakilai a jam’iyyar PDP ya rasu

Date:

Dan majalisar mai wakiltar Jalingo, Yorro, Zing a jihar Taraba, Ismaila Yushau Maihanchi ya rasu.

Rasuwar tasa, ta faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar a babban birnin tarayya, Abuja.

Da yake tabbatar da rahoton, kakakin jam’iyyar PDP, Andeta’rang Irammae, ya ce jim kadan bayan zaben, zababben dan majalisar ya kamu da rashin lafiya kuma yana jinya a Abuja.

Da yake bayyana rasuwarsa a matsayin rashin sa ga jam’iyyarsa, ya ce marigayin ba jam’iyyar kadai za ta yi kewar sa ba, har ma al’ummar jihar baki daya.

Shi ma da yake jawabi, mukaddashin shugaban jam’iyyar, Abubakar Bawa, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rauni ga iyalan PDP a jihar da ma kasa baki daya.

Majiyar dangin ta ce za a sanar da shirye-shiryen jana’izar daga baya.

Zababben dan majalisar da ya fafata a zaben majalisar dokoki ta kasa a karkashin jam’iyyar PDP, ya doke abokan hamayyarsa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, New Nigerian Peoples Party, NNPP da Social Democratic Party, SDP da gagarumin rinjaye.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp