fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Shugabar mata ta jam’iyyar PDP ta koma APC

Date:

Hajiya Yar-Sokoto Jega, shugabar mata ta jam’iyyar PDP mai wakiltar Kebbi ta tsakiya a jihar Kebbi, ta koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Jega ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke jawabi a wajen wani biki a Birnin Kebbi a ranar Laraba.

A cewarta, ta bar jam’iyyar ne saboda rashin adalci da kuma rashin shugabanci na gari.

Jega ta bayyana cewa ta yanke shawarar komawa jam’iyyar APC ne saboda dimbin nasarorin da Gwamna Atiku Bagudu ya samu, inda ta kara da cewa ta koma jam’iyyar ne da magoya baya sama da 800.

“Na shafe shekaru da yawa a PDP, ba su da wani abin da za su nunawa mutane kuma jam’iyyar ta yi watsi da mu.

“Ni ma ina amfani da kudina wajen tafiyar da jam’iyya, amma duk da haka ban ga wani sauyi da jama’ata ba, musamman matan da nake wakilta.

“Kafin sauya sheka na, ina shugabancin kananan hukumomi takwas a karkashin jam’iyyar PDP, na tafi tare da mafi yawan mabiyana,” in ji Jega.

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da Alhaji Abubakar Kana-Zuru, shugaban jam’iyyar APC na jihar; Alhaji Sani Zauro, shugaban kungiyar dattawan APC na jiha; da Alhaji Faruk Musa-Yaro, Mataimakin Gwamnan Jihar.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp